Allah mai girma shine me iko mafi daraja
Sammai na faɗin girman sa tsararraki na bayyana aikin hannuwan sa
Kullu yaumin suna maganar sa dare da rana suna shedar sa
Sa'adda Allah ke halittan sammai.
Ya kuma halicci duniya sai ya siffanta mutum daga turɓayar ƙasa.
Ya hura masa numfashi
Allah mai ƙauna ya halicci maniji da mace acikin siffar sa domin suyi dangantaka da shi.
Da farko haka kuwa suka girmama Allah suka ɗaukaka shi suka yi rayuwar da ta dace tare.
Haka ya cigaba har sai ranar da sheɗan ya jarabci macen ta tsinka daga ƴaƴan itacen da aka hana su ci.
Ta koshi ta kuma baiwa mijin ta shi kuma ya ci.
Yin hakan kuwa ya zama sanadin tawaye da bin nufin kan mutum.
Ta dalilin zunubin nan ne mutum ya rabu da Allah, Allah kuwa ya kore shi daga gonar adinin.
Amma duk da haka Allah ya ƙaunaci ɗan Adam.
Ba son sa bane ya rabu da halittar sa.
Amma kuwa tayaya Allah mai tsarki mai adalci zai kasa sharhanta zunubin ɗan Adam.
A cikin littafi mai tsarki Allah ya bayyana shirin da ya yi na ceton duniya da yayi daga shari'ar sa.
Annabi Ibrahim ne na farko da aka nuna masa wannan shirin.
Mutum ne mai adalci da Allah ya yi aiƙawari zai albarkace shi zai ruɓaɓɓaya zuriyar sa kaman taurari da yashi a gaɓar teku.
Allah ya gwada biyayyar Ibrahim da ya umurce shi ya yi hadaya da ɗan sa.
Ya dogara ga Allah ya yi biyayya da shi.
Da Ibrahim ya ɗaga wuƙar ya yanka ɗan sa sai mala'ikan Allah ya tsaida shi.
Ya san shi mai tsoron Allah ne mai biyayya.
Sai Ibrahim ya ga rago da ƙahonni a sarƙafe cikin kurmi.
Ya kama ya yi hadaya a maimakon ɗan sa.
Ta haka ne Allah ya nuna wa Ibrahim cewa dole ne a yanka rago ko wata dabba makamanciya.
Don shafe zunubban mutum har sai Allah ya kawo cikakkiyar hadaya domin fansar zunubai.
Maimakon zunubi ya raba mutum da Allah hadayar zata maida dangantakan su.
Littafi mai tsarki na cewa akwai wanda zai zo, zai zama cikakkiyar hadaya domin zunuban mutum.
Yanda rago ya ɗauki matsayin ɗan Ibrahim haka mai zuwan zai maye gurbin mutum don samun gafara.
Wasu nace da wannan mai zuwa almasihu.
Wato wanda zai zo ya sulhunta duniya da Allah.
Annabawa sunyi annabcin abubuwa na musamman game da almasihu kafin yazo.
Annabi Ishaya yace haihuwar sa zata zama abar al'ajabi.
Budurwa za tayi juna biyu ta haifi ɗa za'a ce da shi ɗan Allah wato aruhu bata jiki ba.
Annabi Mika ya shaida za'a haifi Almasihu a baitallami.
Annabi Zakariya ya yi annabci sai shiga birnin Urshalima bisa kan jaki.
Yahuza ɗaya daga cikin mabiyansa zai bashe shi.
Annabi Ishaya yace shafaffafe na Allah zai kawo labari mai daɗi ga talakawa.
Ze warkar da masu karaya a zuciyan shi ya kwance ɗ`aurarru.
Cewa lokaci yayi da ubangiji zai ceci mutanen sa.
Wanene almasihu?
Anyi annabi mai suna Yesu.
Wasu sun zaci shine annabawa su kayi zancen sa, ko haka ne?
Ko rayuwar su ta cika annabcin?
Ko yesu yafi matsayin annabi?
Abinda zakaji yanzu labarin yesu ne bisaga shaidun.
Acikin littafi mai tsarki.
Wannan kwaikoyo wani ya cike gurbin Yesu.
Koda yake babu mutumin da ya isa.
Anyi wannan shiri ne domin mu gane mu kuma anfana ta rayuwar Yesu.
Ina rubuta maka ya Tiyofalas.
Al'amuran da suka tabbata a wurin mu.
Don kasan ingancin maganar da aka sanar da kai
Azamanin da Kaisar Augustus yana mulkin Roma
Da kuma Hirdus sarkin Yahudiya
Allah ya aiko malaika Jibirulu wani gari mai suna Nazaret
Gun wata budurwa,
Maryamu
Kadda ki ji tsoro Maryamu
Kin sami tagomashi gun Allah
Zakiyi ciki
Ki haifi Da ki sa masa Suna Yesu.
Ƙaƙa wannan zai yuwa?
Da shike ni budurwa ce?
Ruhu mai tsarki zai sauko maki,
Don haka
Mai tsarkin nan da zaki haifa
Za'a ƙirashi ɗan Allah
Mulkin sa
Babu ma tuƙa
Sai Maryamu ta tafi kasar Yahudiya
Don ta gaida Alisabatu yar'uwanta
Wadda ta ke da juna biyu.
Alisabatu
Maryamu
Ƴar'uwata
Ke mai albarka ce a cikin mata
Ɗan cikin ki ma mai albarka
Danaji gaisuwarki
Jaririn da ke ciki na ya motsa da farin ciki
Zuciyata na daukaka Ubangiji
Ruhuna kuma na farin ciki da Ubangiji mai ceto na
Yanzu tsararraki zasu ƙira ni mai albarka
Yaku mutanen Nazaret
Kaisar Augustus ya yi shelar cewa
A rubuta sunayen da ke zaune ƙasar Yahudiya
Kowa ya tafi a rubuta shi
A jihar sa
Da garinsa na asali
Yusufu da Maryamu sun je Baitalami ta Yahudiya don a rubuta su
Amma basu sami masauƙi a Urshalima ba
Sai suka sauƙa a ɗakin tumaki
Ayankin ƙasar
Wasu makiya na tsaron garken su da daddare
Sai ga mala'ikan Ubangiji kusa da su
Hasken Ubangiji ya haskaka su
Yau a birnin Dauda an haifa mu ku mai ceto
Shine
Almahisu
Makiyayan suka tafi da sauri
Su ga jaririn ƙwance a kwami
Su suka fara kai labarin nan mai daɗi na haihuwar Mai ceto
Da rana ta takwas tayi da za'ayi masa kaciya
Aka sa mai suna Yesu
Yusufu da Maryamu suka kai shi Urshalima su miƙa shi ga Ubangiji.
A Haikalin akwai wani adali mai suna Samilu
Ruhu ya nuna masa bazai mutu ba sai ya ga Almasihu
Ya Allah
Yanzu ka sallami bawanka lafiya
Bisa ga maganar ka
Yanzu naga ceton ka zahiri
Yaron nan zaɓaɓɓen Allah ne
Allah ya albarkaceku
Bayan wasu watanni sai Yusufa da iyalin sa suka koma gidan su a Nazaret.
Alokacin da Yesu keda shekara goma sha biyu
Yusufu da Maryamu suka kaishi Urushalima don idin Faska
Amma alokacin da suke komawa gida a tsammamin su yaron yana tare da su
Ashe Yesu ya tsaya a baya
Sai suka koma birni suna ta neman sa
A rana ta uku suka same shi a haikali zaune tare da manyan malamai da dattiɓai.
Shin ɗan wanene ke tambayoyi haka?
Daga Nazaret ne
Mun zaci yana bin mu
Ku gafarce shi
Masu jin sa sunyi mamaki
Ɗana...
Yaya kayi mana haka?
Ni da baban ka muna ta neman ka duk ran mu a ɓace
Meyasa kuke nema na bakusan wajibi ne inyi sha'anin ubana ba?
Ya koma Nazeret da su
Ya ƙaru da hikima da girma da tagomashi gun Allah da mutane
A shekara ta sha biyar na mulkin Kaisar Tubariyas
Buntus Bilatus yana mulkin Yahudiya
Hirdus yana sarautar Galili
Hanana da Kayafas ne manyan Firistocin
Maganar Allah ta zowa Yahaya a jeji
Yabi lardin kogin Urdun
Yana wa'azi mutane su tuba a gafarta zunubansu
Ku juyo daga zunubanku
Ayi maku babtisma
Allah zai gafarta maku
Yadda yake rubuce a littafin Annabi Ishaya
Murya na kira a jeji cewa
Ku shirya ta farkin Ubangiji
Ku miƙe hanyoyin da zaibi
Za'a cike ko wani kwari
Kowani dutse da tsauni za'a baje su
Za'a miƙe karkatattun wurare
Da gyara munanan hanyoyi
Dukkan ƴan adam
Za suga ceton Allah
Me zamuyi? Gaya mana? Me zamu yi?
Ku mugayen macizai
Me ka keso muyi?
Taimake mu
Gaya mana hanyar da zamubi?
Wanda yake da taguwa
Biyu
Yaraba da wani
Mara
Ita
Duk mai abinci kuma
Ya raba da wasu
Malam
Mu masu karɓan haraji ne
Me zamu yi?
Kar ku karɓi fiye da abunda aka umurce ku
Amma mufa?
Me zamuyi?
Kada ku kwacema kowa kudi
Da ƙarfi
Kada kuma ku zargi wani da karya
Kudai dangana da albashin ku
Gaya mana kai ne Almasihu?
Ni ina maku babtisma da ruwa
Amma wani na zuwa ya fini girma sosai
Ko takalminsa ma ban isa in kwance ba
Zaiyi muku babtisma da ruhu da kuma wuta
Ƙwaryar shiƘarsa na hannun sa
Ya share masussuka ya tara alkama
Yasa a rumbun sa
Ruhu mai tsarki ya sauƙo bisansa da kamannin kurciya
Murya daga sama tace
Kai ne ƙaunataccen ɗana ina murna da kai
Da Yesu ya fara koyarwa yana da shekara talatin
Ya dawo daga kogin Urdun cike da ruhu mai tsarki
Ruhu ya izashi jeji har kwana arba'in, Ibilis na gwada shi a kwanakin bai ci komai ba
Sai Ibilis yace masa
In kai ɗan Allah ne ka umurci dutsen nan ya zama gurasa
An rubuta
Bada gurasa mutum zai rayu ba sai da maganar Allah
Sai Ibilis ya kaishi wani wuri ya nuna masa dukkan mulkokin duniya
Zan baka dukkan wannan iko da daukakar su
Don ni aka baiwa
Na kan iya bawa duk wanda naga dama
In zaka yi mini sujada
An rubuta kayiwa Allah ka sujada
Shi kaɗai zaka bauta wa
Sai Ibilis ya kaishi Urshalima kuma
Ya ɗora shi kan tsororuwar haikali
In kai dan Allah ne ka dira kasa daga nan don an rubuta cewa
zai yiwa mala'ikun sa umurni su kiyaye ka, su tallafe ka don kada kayi tuntube da dutsen
Nassi yace
Bazaka gwada Ubangiji Allahn ka ba
Yesu yazo Nazarat inda aka reneshi
Sannu ƴata, Sannu
Ya shiga haikali ran asabar kamar yadda ya saba
Aka miƙa masa littafin annabi Ishaya
Ruhun Ubangiji yana tare da ni
Domin ya shafe ni in yiwa matalauta bishara
Ya aiko ni inyi shela saki ga daurarru in kuma bude wa makafi ido
In yantar da waɗanda aka danne su
In sanar lokacin Ubangiji yayi na ceton mutanen sa
Umm...gaskiyar ka
Gaskiyar wannan nafsi ta cika yau
Kamar yadda ku kaji
Wannan nafsi ya cika?
Masihu ne kadai zai iya cika wannan alkawarin.
Yaya zamu sani?
Masu shakka kun yi mini karin magana
Likita warkar da kanka
Zaku kuma cemini
Duk abinda munji kayi a Kapernahum
Kayi a nan garin ku
Ina kaya maku
Annabi baya karuwa a garin sa
Da kalmonin nan Yesu ya bayyana kansa
Shi ne Almasihu shafaffe da aka aiko ya ceci mutanen sa
Amma Yahudawa sun ƙi shi
Sun so su jefar da shi ƙasa
Amma ya ratsa tsakiyar su
Ya yi tafiyarsa
Ya nufi wajen Kapernahum a kasar Galili
Al'ummar Romawa ke musu mulkin mallaka
Jama'a kuwa na marmarin zuwan shafaffe na Allah don ya cecesu
Salama gareku
Yawwa
Barka
Jirgin ka zai ɗauken Siman?
Me zai hana
Bazai tafi ba ko?
Yi mana magana
Yi mana magana
Yi magana da mu Yesu
Wasu mutum biyu sun shiga Haikali yin addu'a
Bafarise da kuma mai karɓar haraji
Bafarisen ya miƙe yin addu'a ya ce
Ya Allah nagode da yake ni ba kamar sauran mutane nake ba,
mazambata, marasa adalci, mazinata ko kamar mai karɓan harajin nan
A mako ina azumi sau biyu
Komi na samu nakan fitar da zakka
Mai karbar haraji kuwa ya na tsaye nesa
Bai ɗaga kai sama ba
Ya bugi ƙirjin sa yace
Ya Allah
Kaji tausayina mai zunubi
Kuji
Mai karɓan haraji ya koma gidan sa baratacce
Ba kamar ɗayan ba
Duk mai ɗaukaka kan sa ƙasƙantar da shi za'ayi
Mai ƙasƙantar da kansa kuwa
Ɗaukaka shi za'ayi
Yi gaba da jirgi zuwa gu mai zurfi
Ku saki tarko ku zanyo kifi
Maigida munyi fama dukkan dare
Amma bamu kama komai ba
Amma tunda kace haka
Za mu jefa tarunan
Yakubu, Yahaya
Yakubu, Yahaya ku kawo jirgin ku da sauri ku taimaka mana
Baza mu iya ba
Muna da abunyi
Madallah
Madallah
Rabu da ni ya Ubangiji
Ni mai zunubi ne
Kada kuji tsoro
Yanzu mutane zaku rinka kamowa
Kuzo gareni ku ji magana ta
Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa
Ku kira gareshi tun yana kusa
Masu mugunta su bar al'amuran su
Su juyo ga Ubangiji gama shi ne mai jin ƙai
Mai saurin gafartawa
Kuyi gaskiya da adalci
Zaku kuwa bayyana adalcin sa
Za'abi da ku da salama
Yana zuwa
Gashi nan
Yesu
Yesu
In ka yarda ka ceci ƴata tilo
Yi mana jinkai
Shekarunta sha biyu tana bakin mutuwa in ka yarda kazo muje
Ayya Yairus
Yesu
Ƴar ka ta rasu kar ka wahalar da Malamin
Kada kaji tsoro
Kaba da gaskiya zata warke
Ku daina kuka
Bata mutu ba
Barci takeyi
Ɗiya
Tashi
A bata abinci taci
Na umurceku
Kar ku faɗawa kowa wannan
Bayan haka sai ya ga wani mai suna Lawi dab da ƙofar gari yana karban haraji
Biyoni
Yesu ya hau dutse yin addu'a dukkan dare yana addu'a ga Allah
Da gari ya waye ya gaida sha biyun da ya zaɓe su manzanni
Siman daya bashi suna Bitrus
Da ɗan uwansa Andarawus
Yakubu
Yahaya
Filibus
Batalamowus
Matiyu
Toma
Yakubu ɗan Halfa
Saminu mai suna Zaloti
Da Yahaya ɗan Yakubu
Da Yahuda Iskariyoti maci amana
Albarka ga matalauta
Domin mulkin Allah naku ne
Albabarka ga ku mayunwata don za'a ƙosar daku
Albarka ga masu kuka don zasu yi dariya
Masu albarka ne da mutane suka ƙi ku suka zargeku, suka yi kyamar sunan ku saboda ɗan mutum
Kuyi murna da tsalle a wannan rana
Domin ladar ku me yawa ce a sama
Haka ma kakannin su suka yiwa annabawa
Sha shida, sha bakwai, sha takwas, sha tara, ashirin
Iyakar kenan
Wa yace iyakar kenan?
Kaiton ku masu arziki yanzu
Kun samu taku ta'aziyyar
[Dariya......]
Baya son arziki
Ai ya haukace
Kiton ku masu dariya yanzu
Zaku yi kuka da baƙin ciki
Kaiton ku in kowa na yabon ku
Haka kakannin su suka yiwa annabawan ƙarya
Ina gaya maku masu sauraro ku kaunaci magabtanku
Yiwa maƙiyan ku alheri
Albarkacin masu zargin ku
Yima masu walaƙanta ku addu'a
In wani ya mareka a ɗayan kunci
Juya masa ɗayan kuncin ma
In ya kwace mayafin ka
Ka bashi taguwarka ma
Kaba duk wanda ya roƙe ka
In kuma an kwace kayan ka
Kada ka nemeshi
Kuma yiwa mutane yadda kuke so suma suyi maku
In masoyanku kawai kuke kauna
Wace lada ku ke da ita
Ko masu zunubi na ƙaunar masu ƙaunar su
In mai alheri kuke yiwa alheri
Wace lada ce gareku
Haka masu zunubi suke yi
Ya ya zai taba ta, Yaya zai yi magana da ita
Abin ƙyama
A'a
Ku ƙaunaci magabtanku
Kuyi masu alheri
Ku bada rance banda tsammanin biya
Ladar ku mai yawa ce
Zaku zama 'ya'yan Allah mai girma
Shi me alheri ne ga masu butulci da mugaye
Ku tausaya
Yadda ubanku ke tausayawa
Yesu ka cecemu
Kada ku bada laifi don kar a baku
Kada ku hukunta
Don kada ayi maku haka
Ku yafe
Kuma za'a yafe maku,
Kafishemu ya Ubangiji
Ku bayar
Kuma sai a baku
Mudun da ku ke aunawa da shi za'a auna maku
Makaho
Ba ya yiwa makaho jagora
Ai dukan su biyu sai su fada a rami
Don me ka ke duban haki a idon wani baka kula da gungumen da ke a naka ba?
Ubangiji ka fishe mu
Muna bukatarka yanzu Ubangiji
Mai murna ce mahaifiyar ka da kasha mamanta
Albarka ta tabbata ga masu jin maganar Allah
Suna kiyayewa
Ina so in san mutumin nan
Kana zato shi ne
Almasihu
Bafarise ya gayyacesu cin abinci a gidan sa
Yesu kuwa yaje garin ya zauna ya ci
Yara ku tafi kunji ko
Kunji ni
tafi
Sun iya yin kowace irin fitina
Me ta keyi haka ban sani ba
Me ta keyi
Da shi annabi ne da yasan kowace irin macece ke taɓa shi
Da yasan cewa ita mai zunubi ce
Nasan kowace irin macece Saminu
Saurara kaji
Akwai wani mai bin mutum biyu bashi
Ɗaya tsabar kudi ɗari biyar ɗaya kuma hamsin
Da suka kasa biya
Sai mutumin ya yafe musu dukansu biyu
Wa zai fi kaunarsa acikin su?
Agani na wanda aka yafewa mai yawa
Dai-dai ne
Ka ga matannan
Nazo baka bani ruwan wanke ƙafa ba
Amma ta wanke ƙafafuna da hawayen ta
Ta goge da gashin kanta
Kai baka sumbanceni ba
Tun shigarta bata daina sumbartan ƙafafuna ba
Baka shafa mani mai a kai ba
Ita ta shafa min man ƙamshi a ƙafafuna
Ina gaya maka
Don wannan an gafarta mata zunuban ta duka
Wanda an gafartawa kaɗan
Ƙauna kaɗan ya keyi
An gafarta zunuban ki. (aaah wannan saɓone babban saɓo)
Jeki ban gaskiyar ki ta ceceki
Bada daɗewa ba Yesu ya zazzaga birni da ƙauye ya na wa'azi yana yin bisharar Allah
Sha biyun nan kuwa suna tare da shi da waɗansu mata da aka raba da baƙaƙen aljanu da kuma rashin lafiyar su
Cikin su da Maryamu mai suna Magadariya wadda aka fitarwa da aljanu bakwai
Da Yuwana matar Kuza wakilin Hirdus
Da Suzanatu da kuma wadansu da yawa da suka yi masu ɗawainiya da kayan su
Hirdus sarkin Galili wanda Yahaya ya tsawatawa akan auren matar dan uwansa ya ƙulle Yahaya a kurkuku
Lafiya....... da muka kusanci ƙofar gari Na'im
Mutane suka fito dauke da gawa
Mamacin shi kadai ne ga uwa tasa
Da Yesu ya ganta
Yaji tausayinta
Ya taɓa makarar yace
"Saurayi nace maka ka tashi."
Mamacin ya tashi ya zauna
Yesu ya bada shi ga uwa tasa
Tambaye shi kuce
Kai ne annabi Ishaya yace ke zuwa?
Ko kuwa musa ido ga wani
Megida
Megida
Yahaya mai babtisma ne ya aiko mu
Mu tambaya ko kai ne me zuwan nan
Ko musa ido ga wani
Gayawa Yahaya abinda kun ji kun gani
Makafi na gani
Guragu na tafiya
Albarka ga wanda baya tuntuɓe domina
Ɗora ni a kafaɗar ka
Eeh
Ina ganin Yesu
Eeh inaganin Yesu
Wani mai shuka ya tafi shuka
Yana watsa iri sai wasu suka faɗa a hanya aka tattake su
Tsuntsaye suka tsince irin
Wasu suka faɗa a dutsi
Da suka tsiro sai tsiron suka bushe saboda babu damshi
Wasu kuma suka faɗa a ƙaya
Suka tashi tare amma
Sai ƙayar ta shake su
Wasu suka faɗa a ƙasa mai kyau
sunyi girma sunyi tsaba sosai
Kamar riɓi ɗari-ɗari
Shugaba
Don me ka ke magana da misalai duk lokacin taro?
Kukam an yardan muku
Kusan asirin Allah
Amma ga sauran sai da misali don su gani bazasu gane ba
Su ji bazasu fahimta ba
Ga bayanin wannan misali
Irin
Maganar Allah ce
Waɗanda suka faɗa a hanyan sune masu jin maganar
Sai sheɗan ya dauƙe maganar daga zuciyarsu don kada su gaskanta su samu ceto
Nakan dutse kuwa da zaran sunji maganar sai su karba da farin ciki
Sukam basu da tushe
Sukan gaskata kwanaki kaɗan
Amma in lokacin gwaji yayi
Sai su ridda
Wai'nda sun faɗa a cikin ƙaya sune masu jin magana
Amma yawan taradadin duniya, dukiya da shagalinta sun shaƙe su
Har su kasa yin amfani
Waɗanda aka shuka kasa mai kyau
Sune wadanda suka ji maganar
Suka rike ta kamkam da kyakkyawar zuciya
Suku jure har suka yi amfani
Ba mai kunna fitila ya rufe ta da masaki
Ko yasa a ƙarkashin gado a'a
Sai ya dora a madorinta
Domin masu shiga suga haskenta
Ba abinda ke boye da baza'a bayyana ba
Ba kuma asirin da bazai tono ya zama bayyananne ba
Ku kulafa ku iya ji
Duk mai abu akan ƙarawa
Marar abu kuwa ko abinda yake tsammani yake da shi sai a karɓe daga gurin sa
Malam mahaifiyar ka da ƴan'uwan ka suna waje suna son ganinka
Masu ji suna aikata maganar Allah
Sune ƴan'uwana
Wata rana Yesu ya shiga jirgin ruwa tare da almajiran sa
Yace masu
Mu haye wancan hayin teku
Suna cikin tafiya sai barci ya kamashi
Megida
Megida
Yesu
Hadari zai hallaka mu
Zamu nitse
Ka cecemu ya Ubangiji
Ashe zamu tsira
Ina bangaskiyar ku
Suka iso ƙasar Garasinawa wanda ke ƙetaren tafkin Galili
Yesu dan Allah madaukaki
Ina ruwan ka da ni
Na roƙeka
Karka azabtar da ni
Ya ya sunan ka
Tuli
Ubangiji mun roƙeka
Kada ka wahal da mu
Bari mu shiga
Cikin garken
Garken
Aladu
Kai dawo
Tsaya
Tsaya
Aljanun sun rabu da mutumin sun shiga aladun
Tafi daga nan
Kai matsafi
Rabo damu
Tafi daga wurin nan
Rabu da mu
Tafi daga nan
Zan bika duk inda zaka
Bari
In bika
Koma gida
Ka faɗi abinda Allah ya yi maka
Yesu da almajiransa sun janye jikinsu zuwa Baitasda
Amma taron suka gane
Sai suka bishi.
Chan da rana Bitrus yace
Shugaba
Ka sallami jama'a su tafi kauyuka da Gonaki su samu abinchi da masauki.
Domin nan gurin
Bakowa.
To ku kubasu abinci mana su ci.
Abun da muke dashi kenan gurasa biyar da kifi biyu.
Me albarka ne Ubangiji sarkin sarakuna
Wanda yake bada abinchi daga ƙasa
La abin al'ajabi. Abin mamaki
Wa mutane ke cewa nake
Wasu sunce Yahya me baptisma ne
Wasu kuwa sunce Iliya ne
Wasu kuma suna cewa ɗaya daga cikin annabawan da ne
Ya tashi da rai
To amma kufa
Wa kuke cewa nake?
Almasihu na Allah
Kada ku gayawa kowa wannan
Lallai ne dan mutum zaya sha wuya a ƙishi
Za'a kashe shi
Amma bayan kwana uku zai tashi da rai
Akwai wanda zai iya biyo ni?
Zan bika shugaba
Amma da fari bari inje inyi bankwana da iyalina,
Mai huɗa dake yin huɗa yana dubin baya bai dace da mulkin Allah ba
Duk mai son ya biyoni kuwa sai yaƙi kansa tukuna
Ya ɗauki giciyen sa kowace rana ya biyoni
Duk wanda yake son ransa
Zai rasa shi
Wanda kuma zai bada ransa domina
Tattalinsa yake
Mai mutum zai amfana in ya samu dukkan duniya ya rasa ransa
Wanda ya ji kunyar shaida ni da maganata
Ɗan mutum zaiji kunyar shaidarsa in yazo cikin daukakarsa
Da daukakar uba da ta mala'iku masu tsarki
Ina tabbatar muku
Akwai waɗansu anan cikin ku da bazasu mutu ba sai sunga mulkin Allah
Yesu ya ɗauki Bitrus da Yahaya da Yakubu ya hau dutse yin addu'a
Yana addu'a sai kamanninsa suka sake
Tufafin sa kuma suka yi fari fat
Sai ga mutum biyu na magana da shi
Annabi Musa da Iliya sun bayyana cikin daraja
Zaka cika nufin Allah
Zaka mutu a Urshalima
Annabawan na rabuwa da shi sai Bitrus yace wa Yesu
Shugaba
Yana da kyau da muke nan
Mu kafa bukkoki uku
Ɗaya taka
Yana magana sai gajimare ya rufe su suka tsorata
Sai aka ji muryar zati na cewa
Wannan shi ne zaɓaɓɓen ɗana kubishi
Malam
Malam
Ina roƙon ka ka dubi ɗana
Kaji juyayin sa
Don shi kaɗai ne gareni
Na roƙi almajiran ka su fitar da aljannun
Amma sun kasa
Ya ku tsara marasa ban gaskiya
Har yaushe zan zauna ina ta haƙuri da ku?
Kawo ɗan ka nan
Ya warke fuskarsa tayi haske, abun mamaki
Koya mana addu'a wadda Yahaya ya koyawa almajiransa
Idan kuna addu'a kuce
Ya uba dake cikin sama
A tsarkake sunayenka
Mulkin ka yazo
Mulkin ka ya tabbata a sama da ƙasa
Ka bamu abincin yini
Ka gafarta mana laifofinmu gama muna gafartawa duk wanda yake mana laifi
Kada ka kaimu wajen jaraba
Amma ka cecemu daga mugu
Ku roƙa za'a baku
Ku nema zaku samu
Ku ƙwanƙwasa
Za'a buɗe maku
Wanda ya roƙa akan bashi
Mai nema zai samu
Wanda ya ƙwanƙwasa kofa za'a buɗe masa
Hahaha
Wani uban kirki ne acikin ku
Zaiba ɗan sa maciji
In ya roƙeshi kifi
Ko ya bashi kunama in ya roƙeshi kwai
Kuda kuke miyagu kun iya ba ƴaƴanku masu kyauta kyau
Balle uban ku dake sama, zai bada ruhu mai tsarki ga duk masu rokon sa
Ina gaya muku
Kada ku damu da ranku don abinda zaku ci
Ko kuma jikin ku abinda zaku sa
Domin rai yafi abinci
Jiki kuma yafi tufafi
Kudubi hankaki
Basa shuka ka girbi basu da taska ko rumbu
Amma Allah na cishe su
Saunawa darajarku tafi ta tsuntsaye
Wanene acikin ku don damuwa
Zai ƙara tsawon ransa?
In ba zaka iya abu haka ba
Don me kake damuwa dasaura
Ku duba furanni
Yadda suke girma
Basa shuka ko girbi
Duk da haka ko adon Sulemanu ma bai kai na ɗayan su ba
In Allah
Yana lura da tsire-tsiren jeji wanda yau yana raye gobe a jefa a murhu
Balle ku yan adam da Allah ya baku daraja
Ya ku masu ƙarancin ban gaskiya
Ka ƙarfafa bangaskiyar mu
Da kuna da bangaskiya kamar ƙwayar munsar
Zakuce wa itacen durumin nan
Ciruka dasu cikin teku
Sai kuwa ya bi umarninku.
Dalilan zunubi dole suzo
Amma kaiton wanda shine sanadiyar su
Gara a ratayawa mutumin nan dutsin niƙa a jefa shi cikin take da yasa daya daga cikin ƴan ƴarannan ya yi lefi
Mulkin Allah yana kama da me?
Ya na kama da haka
Wani mutum ne ya ɗauko kwayar munsar ya shuka a lambun sa
Ta girma tayi itace tsutsaye sukayi sheƙar su a rassanta
Bangane abunda yake faɗi ba
Don me kuke ci kuke sha da masu karɓar haraji da masu zunubi
Lafiyayyu ba ruwansu da mai magani sai dai marassa lafiya
Banzo kiran masu adalci don su tuba ba
Sai masu zunubi
Sake gaya mana game da mulkin akwai wani abu kuma?
Kada kuji tsoro ƙaramin garke
Allah na baku rabo a mulki
Ku sayar da mallakarku, kuba matalauta
Ku samu ma'ajin da baya ƙarewa
Kuyi ajiya a sama
Inda ba mai rage ta
Inda ba ɓarawo da zai sata
Ba'a son da zai taɓa
Inda dukiyarka take nan zuciyarka take
Mace
An rabaki da rashin lafiyar ki
Duba, duba ta warke, abin mamaki abin al'ajabi, kuzo ku gani
Ɗaukaka
Ga Allah
Shekaru sha takwas
Allah ya saka maka Malam
Akwai ranaku shida don yin aiki
Kuzo mana a warkar da ku a ranakun
Amma ba'a ranar asabar ba
Munahikai
Ashe kowannen ku baya kwance saniyar sa ko jakin shi ya kaishi ban ruwa ranar asabar
Matannan ƴar zuriyar Ibrahim wadda sheɗan ya daure ta yau shekara goma sha takwas
Ba sai a kwance ta ko ran asabar ba
Malam managarci
Me zanyi domin na gaji rai ma dauwami
Don me ka ƙira ni managarci?
Ai managarci sai Allah kaɗai
Kasan waɗannan dokokin bazakai zina ba
Kada kayi kisan kai
Kada kayi shaidar zur
Ka bada girma ga iyayen ka
Ai na kiyaye duk waɗannan dokoki tun ƙuruciya ta
Har yanzu abu gada ne ya rage maka
Ka sayar da duk mallakarka ka rabama gajiyayyu
Zaka samu wadata a sama
Sa'annan kazo ka bini
Mu fatake ne
Attajirai
Daker nefa masu dukiya su shiga mulkin Allah
Ai zai fiyewa rakumi yabi ta ramin allura
Da mai arziki ya shiga mulkin Allah
Wa zai samu ceto kenan?
Ai abinda yafi ƙarfin mutum zaiyiwu a wurin Allah
A ina wannan zai kasance
Mulkin Allah?
Ai bayyanan mulkin Allah ba ganin sa ake da ido ba
Ba wanda zaice
Duba
Gashi nan ko gashi can a'a
Mulkin Allah a tsakanin ku yake
Lokaci zaizo da za'a fiso ganin rana daya daga cikin ranakun dan mutum
Amma baza ku gani ba
Kamar yadda walkiya takeyi
A bangon duniya haka ɗan mutum zai zama a ranar bayyanarsa
Amman sai yasha wahala tukunna mutanen zamaninnan su kuma ƙi shi tukunna
Zaifi sauki sararin sama da ƙasa su shude da digo daya na attaura ya gushe
Annabawa da sarakuna na son ganin abinda kuka gani amma basu gani ba
Suji abinda kuke ji amma basu ji ba
Toh me zamuyi?
Me nasin yace
Ya ya kuke karantawa
Ka kaunaci Ubangijinka
Da dukkan zuciyarka
Da dukkan ranka
Da dukkan karfinka
Da dukkan hankalin ka
Ka kuma kaunaci makwabcinka [Daidai ne] kamar kanka
Haka zaka rayu
Wanene makwabcina?
Ba dai sojojin nan ba
To Kaisar fa?
Wani mutum ya tashi daga Urshalima zashi Yariko
yan fashi suka fada masa
Suka dake shi har ya kusan mutuwa
Wani firis ya biyo ta wannan hanya
Da ya ganshi
Ya zaga ya wuce
Haka ma wani Balewe
Ya iso wurin ya ganshi
Shima ya zaga ta ɗaya gefe ya wuce
Ana nan sai hanya ta kawo wani Basamariye inda yake
Da yagan shi sai tausayi ya kamashi
Yaje wurin sa
Ya zuba masa mai da ruwan inabi
Sa'annan ya ɗora shi akan dabbar sa yayi ta jinyar sa
Washegari ya ɗebi kuɗi ya ba megidan yayi jinyarsa
Duk kuma abinda ka kashe
Bayan wannan
Sai in biya ka
Cikin ukun nan
Wa kake tsammani ya zama ɗan'uwa ga wanda ƴan fashi suka faɗa masa?
Wanda ya nuna masa jinƙai
Ku ma kuyi haka
Aha
Kubar yara ƙanana suzo guna kada ku hanasu
Ai mulkin Allah na irin sune
Haƙiƙan ina gaya maku
Duk wanda baiyi na'am da mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, bazai shiga mulkin ba
Wanda ya marabci yaro a cikin sunana ya marabceni
Wanda ya marabceni ya marabci wanda ya aikoni
Wanda yake ƙarami a cikin ku shi ne mai girma
Kai meke faruwa, me akeyi?
Yesu Kiriti Banazare ne yake wucewa
Yesu!
Yesu
Yesu ɗan Dauda
Yi mini jin ƙai
Me kake so inyi maka?
In samu ganin gari
Karɓi warkarwa
Ban gaskiyarka ta warkar da kai
Ina gani
Na iya gani
Ina gani
Yesu kama hanya zuwa Urshalima jama'a suka bishi
Suna tambaya yadda zasu samu ceto
Yesu ya yi musu koyarwa gameda mulkin Allah
Lallai mutumin nan annabi ne
Ya Ubangiji ka cece ni
Ubangiji ka cecemu
Yabi Ubangiji
Nuna mana hanyar gaskiya Ubangiji
Mutane su soma yarda da Yesu cewa shine Ubangiji
A Yariƙo akwai wani mutum mai suna Zakka
Ya nemi ganin Yesu harya hau wani durumi [Ina mai karɓan haraji] domin ya ganshi
Zakka maza ka sauƙo
Domin yau a gidanka zan sauƙa
A gida na
Wa zai so ya sauƙa a gidan sa
Ta yaya Zakka ya san Yesu?
Kuji
Zan bada
Rabin mallakata
Wa gajiyayyu
Kowa na
Zalunta kuwa
Zan mayar masa
Da ninki huɗu
Ban gaskantaba
Mai karɓan haraji ya mayar da kuɗi
Basi yiwuwa
Yau kam ceto yasauko a gidannan
Tunda yake mutumin nan ma ɗan zuriyar annabi Ibrahim ne
Ɗan mutum yazo neman abin da ya ɓata
Kuji
Zamu Urshalima abin da ke rubuce game da ɗan mutum zai tabbata
Gama za'a basheshi ga al'ummai
Kuyi masa ba'a
A wulaƙantashi a kuma tofa masa miyau
Su bulaleshi, su kashe shi
Amma ranar
Ta uku zai tashi
Yesu ya san cewa za'a kashe shi domin zunuban ƴan Adam
Amma yayi gaba zuwa Urshalima
Mutane da yawa sukai murna, sukace da shi sarkinsu
Malam
Kwaɓi almajiran ka suyi shiru
Koda almajiraina sun yi shiru
Duwatsunnan ma sai su ɗauki sowa
Ranka yadade
Da Yesu ya hangi Urshalima yayi juyayin birnin da mazaunan sa
Dama ace
Kunsan hanyoyin da ke kawo salama yanzu boye suke gareku
Raneku na zuwa da mikiyan ku zasu muku kawanya suyi maku zobe su matseku ta kowani gefe
Tsakanin nan ne zasu halaku
Kuda ƴaƴan ku
Baza subar wani dutse akan wani a birninku ba don basu gane irin alherin da an sauƙar maku ba
Haikalin dake Urshalima ya zamo wurin ciniki maimakon gidan sujada
Ɗaya, biyu, uku, hudu, biyar, shida, bakwai, takwas, tara, goma, sha ɗaya, sha biyu, sha uku,
sha hudu, sha biyar, sha shida, sha bakwai, sha takwas, sha tara, ashirin, ashirin da daya, ashirin da biyu
A rubuce yake
Gidana zaya zama gidan addu'a
Amma ku kun maishe shi kogon mafasa
Dubi
Ya nufi dabbobina
Tsare shi
Tsare shi
A kira ƴan tsaro
A kira ƴan tsaro
Gardama ta tashi tsakanin wasu shugabannin siyasa da na addini
Don mutane nacewa Yesu sarkine
Nagane cewa mutane na ɗaukaka shi kamar sarki
Sarki
Sarkin maroƙa, karuwai da ɓarayi
Munsha ganin irinsu
Zasu zo su sheƙa ayarsu su tafi
A manta da su
Karka ruɗe
Mabiyansa ƙaruwa sukeyi kullum
Yana da farin jini garesu
Cewa shi sarki ne
Toh bari in gargarɗe ku
In mutumin nan ya cigaba da tada husuma
Kune zan hukunta
Gaskiya nefa
Yakamata mu tuhumeshi
Sa'adda sashin ƴan riya da Farisiyawa suke ƙara tsanantawa Yesu
Farisiyawa masu binsa cikin Yahudawa na ƙaruwa
Haka kuma masu gaba da shi waɗanda ya kayar
Ɗan kadan ne
A hailkali Yesu yaga wata gauruwa ta saka anini biyu cikin tasa
Baki ƙarawa?
Ina gaya maku
Abinda gwauron nan tasaka yafi na kowa
Domin waɗannan duka
Sun bayar daga yalwar su ne
Cikin rashinta ta bada dukkan mallakanta
Gayamana
Da wani izini kake faɗin abubuwannan
Wa yaba ka izinin?
Nima zanyi maku tambaya
Wai babtismar Yahaya
Ta Allah ce ko ta mutum ce?
To me zamu ce
In munce daga sama take
Zaice to don me
Bamu gaskanta da shi ba
In munce ta mutum ce sai jama'a su jejjefe mu
Don sun tabbata
Yahaya annbi ne
Bamu san inda ya fito ba
Bazan faɗa maku koda wani izini nake aiki ba
Wani mutum ne yayi gonar inabi
Yaba manoma aronta
Ya tafi wata ƙasa ya daɗe
Da amfanin gonar isa girbi
Ya aiki bawansa gun manoma
Domin su bashi nashi rabo daga gonar
Manoman sukai masa duka ya koma hannu wofi
Sai ya aiki wani bawa
Shima sun masa duka
Suka walaƙanta shi suka koreshi hannu wofi
Sai ya aiki na uku shima sunyi masa rauni
Suka koreshi sai mai gonar yacema kansa
Me zanyi kenan?
Zan aiki ƙaunataccen ɗana
Haƙikan zasu bashi girma
Amma da manoman suka ganshi sai sukace ga junansu
Ai wannan shine magajin
Mu kashe shi sai gadon ya zama namu
Ka cigaba
Sai suka fidda shi daga gonar
Suka kashe shi
Me kuke zaton ubangijin nan zaiyi da manoman
Zaizo ya hallaka mugayen manoman nan ya ba wani gonar
Menene nasin nan ke faɗi?
Dutsin da magina suka ƙi shi ne ya zama
Dutsi nafi muhimmanci na gini
Dukkan wanda ya faɗa akan dutsin nan sai ya ragargaje
Amma wanda dutsin ya faɗawa
Niƙe shi zaiyi kamar gari
Malam
Mun san cewa koyarwarka gaskiya ce
Ka ɗauki kowa dai-dai babu banbanci sai dai koyar da tafarkin Allah dai dai ka keyi
Gayamana
Dai-dai ne bisa ga shari'a mu biya haraji ga mai mulkin Roma
Ko kuwa?
Ubangiji yi hankali da su dai
Fito da kuɗin mugani
Hoton wa da sunan wa kega kuɗin
Kaisar
To sai kuba Kaisar
Abinda kena Kaisar
Kuba Allah
Abinda kena Allah
To yanzu me zakuce?
Bukin gurasa mara yisti wanda ake ƙira idin ketarewa ya kusa
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya domin su shirya idin ƙetarewa
Naso cin abincin idin ƙetarewa daku ƙwarai kafin in sha wuya
Ina gaya maku
Bazan ƙara cinsa ba sai an bada cikakkiyar ma'anarsa a mulkin Allah
Mai albarka ne kai Allan mu
Sarkin halitta
Mai bada abin sha daga ƴaƴan itace
Karɓi wannan ku raba tsakanin ku
Ina gaya maku bazan ƙara shan ruwan inabin ba sai mulkin Allah ya bayyana
Mai albarka ne kai ya Allan mu
Sarkin halitta
Wanda yake kawo abinci daga ƙasa
Wannan jikina ne da za'a bayar domin ku
Ku riƙa yin haka don tunawa da ni
Ƙoƙon sabon alkawali ne daga jinina da an zubar domin ku
Gashi mai basheni ɗin nan yana ci a akwashi ɗaya tare da ni
Lallai ɗan mutum zai ƙaura kamar yadda an kaddara amma kaiton mutuminnan mai bashe shi
Ko nine?
Tambaye shi wanne yake nufi
Ubangiji!
Wane ne?
Wanene munafukin ya Ubangiji?
Babba acikin ku ya zama kamar ƙarami
Shugaba ya zama kamar mai hidima
Wa yafi girma?
Wanda ya zauna cin abinci ko mai hidimar?
Wanda ya zauna mana
Gashi ina cikin ku kamar mai hidima
Tare muke cikin wahaluna
Kamar wadda ubana ya bani mulkin
Haka ni nake baku ikon
Zaku ci ku sha tare da ni a mulkina
Zaku zauna a kursiyay ku mulki ƙabibun Isra'ila sha biyun
Ashe ba munafikin ma
Siman Siman kaji
Sheɗan ya nemi izini ya gwada ku
Ya sheƙe ku kamar yadda manomi ya ke sheƙe alkamar sa
Nayi addu'a kada bangaskiyarka ta kasa Siman
Bayan ka juyo wuri na ka ƙarfafa ƴan'uwan ka
Ubangiji ina shirye in bika har kurkuku
Har ma mu mutu tare
Haƙiƙa Bitrus yauma kafin charar zakara zakai musun sanina sau uku
Da na aikeku ba kuɗi ba jikka akwai abunda kuka rasa
Babu. Ko kaɗan
Amma yanzu duk mai kuɗi ko jikka ya ɗauka
Wanda bashida komai ya saida mayafinshi ya saya
Ina gaya maku
A rubuce yake cewa an lisafta shi cikin masu laifi
Abinda an faɗa a kaina ya tabbata
Duba
Ga takuba biyu Ubangiji
To ya isa
Sai shugabannin sukayi shawara akan yadda zasu kashe Yesu
Sai sheɗan ya shiga Yahuza dan Iskariyoti daya daga cikin sha biyun
Ya gama baki da shugabannin don kama Yesu
Yesu yabar Urshalima zuwa dutsen zaitun don yin addu'a
Kuyi addu'a don kada ku faɗa ga gwaji
Yahudu Iskariyoti ya sayar da Yesu kan kuɗi azurfa talatin
Yasan lokacin mutuwarsa don zunuban ƴan adam yayi sai yayi addu'a
Ya uba
Indai ka yarda
Ka ɗauke mini wahalan nan
Duk da haka
Ba nufina zaɓi ba sai dai naka
Mala'ika ya bayyana gareshi don ƙarfafa shi
Har jikinsa na ɗiɗɗiga kamar manyan ɗiɗɗigar jini
Don me kuke barci
Ku tashi
Kuyi addu'a kada ku shiga cikin jaraba
Yahuda
Da sumba ne kake son ka bada ɗan mutum
Ubangiji mu sara da takobi ne?
Ku kama shi
Ya isa haka
Abun al'ajabi
Kunzo da tokubba da kulake kamar masu kama dan fashi
Da nake tare daku cikin Haikali baku kamani ba
Amma wannan zarafin kune
Dana mulkin duhu kuma
Ku kamashi
Tare shi da kyau
Sojojin suka kaishi cikin fada sukayi ta masa ba'a
Ga rigar da sarki yasa
Yi anabci me zai faru
Zaka cecemu ko ranka shi daɗe ai zaka cecemu
Mutumin nan na tare da Yesu
Ke
Ni banma san shi ba
Na gansu tare
Gamunan talakawan ka
Yaya ka kaji yanzu a hannun wani
Kaima tare da su kake
A'a bana cikin su
Ba shakka mutumin na tare da Yesu don shima Bagaliline
Gafara nan
Nifa bansan
Abinda kake cewa ba
Sai Yesu ya juya ya dubi Bitrus
Bitrus kuwa ya tuna da abinda Ubangiji yace
Yau kafin charar zakara zaka yi musun sani na sau uku
Ya Ubangiji nayi maka laifi ka gafarta mani na roƙe ka ka gafarta mini laifina
Ubangiji
Mai jinƙai
Kayimini jinƙai
Naga kasawata a gabanka
Ya mai jinƙai
Mai jin kukan masu laifi
Kaji kukana da roƙona
Na tuba
Na tuba
Ka yafe mini
Bazan ƙaraba kuma ba
Saboda jinƙan ka
Ina rokon ka
Ina rokon ka gafara
Wa ya bugeka
Yi annabci
Wazai sake bugunka
Ku bari!
Ku bari nace
Ku kawoshi yanzu gaban majalisa
Muje!
Ƴan majalisa sun taru don suyiwa Yesu shari'a
Gaya mana
Kai ne Almasihu?
Ko na gaya maku
Baza ku gaskantani ba
In nayi tambaya
Bazaku bani amsa ba
Amma nan gaba ɗan mutum zai zauna a hannun dama na Allah mai iko duka
Wato
Kai ɗan Allah ne?
Kun faɗa nine
Saboda me zai faɗi haka wa ya bashi ikon faɗar haka, ina ya samu ikon fadar haka? Oho
An tabbatar da laifin sa
Muma munji abunda yace
Zamu kai shi gaban Bilatus
ku tafi da shi kaishi wurin Bilatus shi zai hukuntashi
Yi gaba
Suka kai shi gaban sarki Bilatus wanda yafi dukkan sauran gwamnoni mugunta
Shi kaɗai ya giciye dubban mutane
Shin me kuke so anan
Da sassafe haka
Mun samu mutumin nan yana ɓadda jama'an mu
Ya tada hankalin jama'a a majami'a
Wani hukunci za ayi masa?
A hukunta shi
Ban iske mutumin da wani laifi ba
Babu dalili
Mun sameshi da laifi
Yana hana a biyawa Kaisar haraji
Yace shine almasihu
Sarki
Sarki?
Kai ne sarkin Yahudawa?
Haka ku ka ce
Ya faro a Galili
Yanzu gashi yazo nan
A Galili
Mutumin Bagalili ne?
In haka ne
Hirdus ya shar'anta shi
Yana nan a Galili ko kuwa bashi
Kai shi wurin Hirdus
Wanene kai
Mai ka ƙira kanka
Su waɗanne ne ka ke ce da su almajiran ka?
Mutane da yawa sunce kana iya aikin al'ajabi
Kayi mini
In gani
Ya mai girma
Mutumin nan na ɓadda jama'ar mu
Ya ce da kansa
Sarki
Wannan mutum?
Sarki?
Ranka ya dade
Buge shi sosai
Komar dashi gun Bilatus
Wannan yankin ƙasar suce
Wannan mutum baiyi laifin da ya isa mutuwa ba
Saboda haka mayi masa bulala
Sa'annan a sake shi
Muna so a sakar mana da daurarre guda a lokacin idin nan
Sakar mana
Barabas
Ea Barabas
Tafi da mutumin nan
Ea sakar mana Barabas
A gicciye shi
Ea
A giciye shi
Kai
Kai kuyi masa bulala
Sarki Bilatus
Me ka ke jira
Yesu ne
Me yasa kuke wahal da shi?
Wai shi ɗan Allah ne
Kubar shi shine Almasihu
Baiyi komai ba
Ku ɗaga shi
Mutane suka yita ihu da karfi suna cewa a giciye shi
Bilatus ya yankewa Yesu hukuncin kisa
Ya sakar musu da Barabas da aka jefa a kurkuku kan laifin tawaye da kuma kisan kai ya bada Yesu a giciye
Baya koma baya , baya, baya can, matsa daga gun sa
Ja baya
Ja baya
Baya
Sarari
Bada wuri
Fita
Kai bada wuri
Tafi ina gaya maka
Tashi tsaye, tashi tsaye
Kai
Ya sunan ka?
Saminu Bakurani
Zo kusa nan
Yanke igiyar
Ka sauƙe shi
Muje gaba
Baya
Baya
Barshi
Yi gaba
Ku bada wuri can
Koma baya
Koma baya
Munyi kuka domin ka Ubangiji
Sha wannan
Sha
Sha Ubangiji
Matan Urshalima kubar yi mini kuka
Kuyi kuka don kanku da kuma ƴaƴan ku
in abubuwa irin wadannan zasu iya faruwa da danyen itace
Mai zai faru in ya bushe?
Allah ya taimake ka
Zamu yi maka addu'a
Tafi
Ƙasa nan
Bini
Maza
Maza
Kai tafi
Muje
Bisu maza
Bini
Maza
Yanzu tafi
Tafi
Yanzu kai yi gaba
Bini yanzu
Cigaba da shi
Ɗaga
Kai baka ƙusar
Cire igiyar
Uba ka gafarce su
Don basu san abunda suke yiba
Ya ceci waɗansu
Ya ceci kansa mana
Yauwa
Ceci kanka in kai Almasihu ne
Sauƙo daga giciyen
Nuna aikin ka da mujiza
Aka giciye Yesu tsakanin barayi biyu don a cika annabci yadda annabawa suka fada a shekarun baya
Ku gani wannan ba rigar banza bace
Aka sa alama kan giciyen cewa shi ne sarkin Yahudawa
Ceci kanka in kaine sarkin Yahudawa
Ba
Kaine
Almasihu ba
Ceci
Kan ka
Da mu mana
Ko
Tsoron Allah
Baka ji
Mun karɓi
Hukunci
Dai-dai da shi
Naka
Dai-dai ne
Amma mutumin
Baiyi laifi
Ka tuna da ni ya Yesu
Sa'adda ka shiga
Mulkin ka
Ina gaya maka
Yau zaka kasance a aljanna
Tare da ni
To da tsakar rana ne kuwa sai duhu ya rufe kasar har karfe uku na yamma
Labulen cikin Haikalin ya tsage kashi biyu
Ya uba
Na mika ruhu
A cikin
Hannun ka
Da jarumin ya ga abinda ya faru sai ya girmama Allah yace
Alhamduka Allah
Lallai mutumin nan mai adalci ne
Yusufu mutumin Armatiya ɗan majalisa ne kuma adali
Bai yarda da hukuncin da akayi ba yaje wurin Bilatus ya roƙa a bashi gawar Yesu yasa a kabari kafin ranar sujada
Ka yafemu
Munzo gun gawar Ubangijin mune
Ana marabtan kowa
Kuyi sauri
Ranar asabar na gabatowa
A ranar farko ta mako da asussuba suka je kabarin da kayan Ƙamshin da suka shirya
Sun tarar an mirgina dutsen a bakin kabarin sun shiga basu samu gawar Yesu ba
Ayy ya tashi
Ku tuna ya gaya muku tun yana Galili cewa
Lallai ne a bada ɗan mutum ga hannuwan mutane masu zunubi
A giciye shi
Rana ta uku kuma
Ya tashi da rai
Kuji
An mirgina dutsen
Mun shiga
Mun tarar gawan Ubangiji
Bata
Nan
Mene?
Babu gawar Ubangiji
Sai mutum biyu suka bayyana
Mala'iku na haske
Kamar rana
Suka ce mana
Don me kuke neman mai rai
Cikin matattu
Gaskiya ne
Gaskiya ne
Ba ƙarya ba
Mun gansu
Kuje ku gani ba Yesu a kabarin
Ta tashi
Bitrus
Gaskiya ne
Yesu ya bayyana ga biyu daga cikin almajiran da murna suka komo gun saura
Lallai Ubangiji ya tashi
Harya bayyana ga Sima
Bamu gane da shi ba
Akan hanya
Da ya gutsura gurasa
Mun gane shi
Imawus
AbIn mamaki me ya kaishi
Salamu'alaikum
Don me kuka firgita?
Don me kuke da shakka a zuciyar ku?
Duba
Hannuwa na da ƙafafuwa na
Taɓa ni mana
Ay nine
Ay nine da kai na
Ay fatalwa bata da tsoka da ƙashi kaman yadda nake dasu
Wannan ita ce maganata da na gaya muku tun muna tare
Lallai ne a cika abinda ka game da ni a attaura ta Musa littattafan annabawa da zabura
Haka yake a rubuce
Lallai ne Almasihu yasha wuya
A rana ta uku ya tashi da rai
A kuma yiwa
Al'ummai wa'azi su tuba a gafarta musu zunuban su saboda sunan sa
Za'a fara daga Urshalima
Kune shaidun waɗannan abubuwa
Gashi na kawo muku abunda ubana ya alkawarta
Ku dakata a birni tukuna
Har ayi muku baiwar iko daga sama
Allah ya albarkace ku ya tsare ku
An mallaka mani iko a sama da ƙasa
Kuje ku koyawa al'ummai
Kuna musu babtisma da sunan Uba da Ɗa dana Ruhu Maitsarki
Kuna koya masu
Su kiyaye abinda na umurce ku
Gashi ni kuma kullum ina tare da ku har ƙarshen zamani
Ameen
Cikin littafi mai tsarki Allah ya shaida Almasihu zaizo ya ceci dukkan duniya
Rayuwar Yesu ta shaida lallai shi ne annabawa suka yi zancen zuwan sa
Annabi Ishaya yace wata budurwa zata yi ciki ta haifi ɗa
Bayan shekaru da dama haihuwar Yesu ta cika wannan annabcin
Littafi mai tsarki yace mai tsarkin nan da za'a haifa za'ace da shi ɗan Allah
Wato za'a kira Yesu ɗan Allah ba ɗa na jikiba amma ɗa na ruhu
Hakan ya bayyana ta wurin rayuwarsa
Ya warkar da masu cuta
Ya gafarta zunubansu ya shirya su da Allah
Ya kuma alƙawarta musu mulkin Allah na har abada
Ya bada kansa hadaya domin zunuban su ya tashi daga matattu
Yesu yace ba me karɓe mini rai don kaina nake bada shi
Rayuwar Yesu ta cika annabcin annabawa ta kuma ƙarfafa gaskiyar maganar Allah
Annabawa sun shaida cewa
Maganar abar dogara ce kuma tabbatacciya ce ya Ubangiji
Yesu yace sama da ƙasa zasu shuɗe amma maganata bazata shuɗe ba
Yesu ya zo ya bamu rai a yalwace
Ganin yadda mutum ya yiwa Allah rashin biyayya a gonar adinin
Mutum ya zaɓi bin hanyar sa wacce ta rabasa da mahaliccin sa
Littafi mai tsarki yace
Ƴan Adam duka sunyi zunubi
Sakamakon zunubi kuma mutuwa ne
Wato mutuwa ta ruhu kenan
Kamar yadda Allah ya tanada rago a maimakon ɗan Ibrahim
Haka Allah ya aiko Almasihu ya mutu a madadin mu
Rayuwa da mutuwa da tashin sa sun mai da dangantaka tsakanin Allah da masu dogara ga Yesu
Yanzu masu bin Yesu ba gafarta zunuban su kaɗai akayi ba
Amma an cecesu daga hukunci
An tabbatar musu da shiga aljanna
Rai da yanci daga ikon zunubi ne Yesu keba kowa a yau
Ba bin wani addini ba amma ana zancen gaskata Yesu wanda yace
Ganinan tsaye a bakin kofa ina ƙwanƙwasawa
Kowa yaji murya ta ya bude kofar sai in shiga wurin sa
Ana nufin mu juyo ga Allah mu dogara ga Yesu ya shigo zukatan mu
Ya gafarta mana ya maishe mu karɓaɓɓu gareshi ba abin marmari ko tunanin sa a zuciya kaɗai ba
Karɓarsa zamu yi da son ran mu ta wurin alheri saboda ban gaskiya
Duk wanda keso yazamo mai bin Yesu Almasihu zai iya magana da shi cikin addu'a
Mai yuwa kana shirye ka buɗe kofar zuciyar ka zaka iya yin wannan addu'ar a cikin zuciyar ka
Ya Yesu
Ina bukatarka
Nagode da mutuwar da kayi don zunubai na
Na furta zunubai na da roƙon gafara
Na buɗe zuciyata na karɓe ka kazamo mai ceto na da Ubangiji na
Nagode domin gafarar zunubai na domin ka bani rai na har abada
Ka maishe ni irin mutumin da ka keso
Yanzu da na zamo cikin masu binka
Ameen
Yesu yayi magana kan masu binsa da cewa
Tumaki na sun san murya ta na sansu suna bina
In masu bin Yesu suna so su samu rai da ya alkawarta
Dole ne suyi addu'a suna karatu da sauraran maganar Allah kullum
Suyi ta zumunci da juna suna shaida shi ga wasu
Tuna da alƙawarin sa
Cewa an mallaka mini iko dukkan sama da ƙasa
Gashi ni kuma ina tare da ku har matuƙar zamani